--
Yanzu Yanzu: Ana musayar wuta tsakanin Boko Haram da sojoji a Borno,

Yanzu Yanzu: Ana musayar wuta tsakanin Boko Haram da sojoji a Borno,


Ana musayar wuta tsakanin mayaƙan da ake zargi Boko Haram da sojoji a garin Damasak na jihar Borno.





Wata majiya daga sojoji ta ce mayaƙan sun ɗage akan sai sun ƙwace garin Damasak - Wani jami'in tsaron sa kai na Civilian JTF ya tabbatar da cewa an shafe tsawon sa'a uku ana bata
kashi da mayakan A yanzu haka, wasu da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne suna cikin artabu da sojoji a Damasak da ke jihar Borno.





Sojojin sun fatattaki masu tayar da kayar bayan daga garin amma sai suka dawo da safiyar ranar Laraba, suna harbi ba kakkautawa sannan suna cinnawa gidaje wuta.





A cewar wata majiyar sojoji, maharan na matukar neman karbe ikon garin, jaridar Daily Trust ta ruwaito. “Zan iya tabbatar da cewa sojoji ke da iko da garin Damasak amma ana ci gaba da fafatawa. Kun san tsawon wani lokaci yanzu, yan ta’addan sun addabi garin Damasak amma ba za su iya yin nasara ba saboda sojojin mu na nan a kasa,” in ji majiyar.





Haka kuma wata majiya ta JTF ta tabbatar da cewa an kwashe kusan awanni uku garin na karkashin hari. "Akwai bukatar dukanmu mu yi addu'a domin sojojinmu su yi nasara a kan wadannan mugayen mutane, Boko Haram sun koma Damasak bayan harin Asabar, kawai mu yi wa sojojin addu'a," in ji shi.





Wasu yan ta’adda sun kai hari a Damasak a karshen makon da ya gabata kuma akalla mutane shida aka kashe yayin da aka kona wasu gine-ginen jama'a.





Source: Legit


Related Posts

0 Response to "Yanzu Yanzu: Ana musayar wuta tsakanin Boko Haram da sojoji a Borno,"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?