--
Da duminsa: Mataimakin Shugaban Karamar Hukuma Ya Mutu A Kano

Da duminsa: Mataimakin Shugaban Karamar Hukuma Ya Mutu A Kano


Mataimakin shugaban Karamar Hukumar Ungogo a jihar Kano, Alhaji Abdullahi Dantalata Karo ya rasu.





Shugaban Karamar Hukumar, Injiniya Abdullahi Garba Ramat ne ya sanar da rasuwar a shafinsa na Facebook ranar Litinin.





Ya ce, “Innalillahi Wa’inna Ilaihi Raji’un. Allah ya jikan Alhaji Abdullahi Dantalata Karo (Mataimakain Shugaban Karamar Hukumar Ungogo). Allah ya gafarta masa kura-kuransa, ya kuma ba iyalansa hakurin jure rashinsa, mu kuma ya sa mu yi kyakkyawan karshe.”





To sai dai sanarwar ba ta fadi musabbabin rasuwar tasa ba.





Rahotanni dai sun ce za a gudanar da jana’izarsa ranar Litinin a Kano.





Kafin rasuwarsa, marigayin shine ke rike da mukamin Mataimakin shugaban Karamar Hukumar ta Ungogo, kuma ya taba zama shugaban jam’iyyar APC mai mulki na yankin Karamar Hukumar .





Ya kuma taba tsayawa takarar shugabancin Karamar Hukumar, kafin daga bisani a yi maslaha ya tsaya a matsayin mataimaki.





Source: Daily Trust


0 Response to "Da duminsa: Mataimakin Shugaban Karamar Hukuma Ya Mutu A Kano"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?