--
Ta zare N200,000 daga Banki ta shiga Keke napep,an kasheta aka kwace kudinta

Ta zare N200,000 daga Banki ta shiga Keke napep,an kasheta aka kwace kudinta


Wasu da ake zargin yan fashi ne sun kashe wata mata bayan ta zari kudi N200.000 daga Banki ta shiga Keke napep a Birnin Warri na jihar Delta ranar Litinin 15 ga watan Fabrairu.



Wani ganau ya ce matar mai suna Felicia, ta zaro N200,000 ne daga Banki, sai ta tare Keke napep ta shiga, amma bayan yar tafiya, sai wadanda ke cikin Keke napep suka harbe ta da bindiga a kafa, suka kwace mata kudin kuma suka turota kasa suka gudu.


Mun samo cewa an garzaya zuwa Asibiti da Filicia, sai dai Likita ya tabbatar da mutuwarta lokacin da aka isa da ita Asibitin.


DAGA ISYAKU.COM


Kukaranta sabbin labarai anan 

https://www.bzglobalservice.com.ng/

Domin sauke manhajar labaran Bz News24/7 a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=bz.globalservice7

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta: 

Facebook:https://web.facebook.com/bzlabari24 

Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: 

bzglobalservicelabari@gmail.com

0 Response to "Ta zare N200,000 daga Banki ta shiga Keke napep,an kasheta aka kwace kudinta"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?