--
An tsinci kwarangwam kai a unguwar Malala a Birnin kebbi jihar Kebbi

An tsinci kwarangwam kai a unguwar Malala a Birnin kebbi jihar Kebbi


An tsinci kwarangwam na kan mutum a unguwar Malala da ke garin Birnin kebbi babban Birnin jihar Kebbi ranar Talata.


Sai dai bayanai daga majiya mai tushe sun ce kwarangwam da aka samu na wata yarinya ce mai suna Wasila diyar Bala Mai tiles wacce ta bace kimanin wata daya da ta gabata a unguwar Malala.



Bayanai sun ce wani yaro mai bola jari ne ya gano wannan kwarangwam wanda aka lullube da gyale aka bizine.


Bayan da labarinya bulla, mahaifin yarinyar ya shaida gyalen diyarsa da ta bace tana sanye da shi.


Tuni dai jami'an tsaro suka fara bincike kan lamarin kamar yadda wata majiya ta shaida mana.




Kukaranta sabbin labarai anan 

https://www.bzglobalservice.com.ng/

Domin sauke manhajar labaran Bz News24/7 a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=bz.globalservice7

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta: 

Facebook: https://web.facebook.com/bzlabari24 

Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: bzglobalservicelabari@gmail.com

0 Response to "An tsinci kwarangwam kai a unguwar Malala a Birnin kebbi jihar Kebbi"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?