--
Uwa da 'ya'yanta biyu sun kone kurmus a Bauchi Duba dalili

Uwa da 'ya'yanta biyu sun kone kurmus a Bauchi Duba dalili


Wata uwa da ‘ya’yanta biyu sun kone kurmus a wata gobara da ta tashi a ƙauyen Riban Garmu, Unguwar Dewu da ke cikin Karamar Hukumar Kirfi a Jihar Bauchi. 


Wasu mutane hudu sun samu raunuka a gobarar da ta lalata gidan mai dakuna hudu kuma a yanzu haka suna karbar kulawa a Babban Asibitin Kirfi.


Shafin LindaInkeji Ya Wallafa,  An tattaro cewa gobarar ta afku ne sakamakon tartsatsin wutar da ke gidan yayin da dangin ke bacci.


A cewar wani ganau, uwar da ‘ya’yan nata suna ta kururuwar kuka suna neman taimako amma duk kokarin da aka yi na tilasta kofar gidan a bude domin kubutar da su ya ci tura. 



Dan majalisar mai wakiltar mazabar Kirfi a majalisar dokokin jihar, Hon. Abdulkadir Umar Dewu, ya kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan mamatan a madadin Gwamnan Jihar, Bala Mohammed. Ya gabatar da kyautar kudi N250,000 ga dangin a madadin Gwamna.







0 Response to "Uwa da 'ya'yanta biyu sun kone kurmus a Bauchi Duba dalili"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?