--
Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje

Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje

Hssaini Mairiga, shugaban tsagin jam'iyyar APC a jihar Kano, ya sanar da sauke daya tsagin da ke karkashin jagorancin Abdullahi Abbas 


Mairiga ya ce Abbas da sauran mukarrabana sun samu shugabanci ne ta barauniyar hanya - Kazalika, ya gargadi ma su burin shiga takarar zaben kananan hukumomi su guji siyen fom din takara daga wurin shugabancin Abbas 



Wani tsagin jam'iyyar APC a jihar Kano, a karkashin jagorancin Hussaini Isa Mairiga, ya sanar da sauke shugabannin tsagin jam'iyyar a karkashin jagorancin Abdullahi Abbas, kamar yadda Thecable ta rawaito. 


An sake zaben shugabannin tsagin jam'iyyar APC da ke karkashin jagorancin Abbas a shekarar 2018 saboda rikicin da ya dabaibaye jam'iyyar a shekarar 2017. Tsagin da Abbas ya ke jagoranta shine mai daurin gindin gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar ganduje. 


Da ya ke magana da manema labarai a ranar Alhamis, Mairiga ya ce Abbas da sauran mukarabbansa sun karbi shugabancin APC ne ta barauniyar hanya, ta hanyar zaben da ya raba kan mambobin jam'iyya.


"Ta hanyar zaben bogi Abdullahi Abbas ya zama shugaban jam'iyya, amma duk da hakan, ya gaza tabuka komai bayan mulkin kama karya. 


"Ba halastattun shugabanni bane, shugabancinsu ya sabawa kundin tsarin mulkin jam'iyya, a saboda haka duk wani abu da ya fito ta karkashinsu haramtacce ne. "Abinda na ke nufi a nan shine; duk wani dan takarar a zaben kananan hukumomi da za'a yi a watan Janairu kar ya sayi fom din takara ta hannun haramtattun shugabanni. 


"Duk Wanda ya shiga takara ta hannunsu ya shiga asara don ko ya ci zabe sai an kwace a kotu," a cewarsa. A karshe Mairiga ya bukaci shugabancin APC na kasa ya kafa kwamitin riko na jam'iyyar a jihar Kano domin ya gudanar da sabon zaben shugabanni na gaskiya.


SOURCE: LEGIT


Mtn Data Bonanza By Bz Global Services 🌐

1GB @N350 

2GB @N700

3GB @N1,050

4GB @N1,400

5GB @N1,750

Validity For 30Days

Hanyar Biya Bank Transfer Domin Siya Yanzu Kiramu Ta Number Waya 08133888333 Koka Aiko Sako Ta Whatsapp: 09066633320


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?