--
Kalli Hotunan wani Yanki A jihar Adamawa inda jama'a ke shan ruwa daya da dabbobinsu

Kalli Hotunan wani Yanki A jihar Adamawa inda jama'a ke shan ruwa daya da dabbobinsu

Da rashin muhimman gine-gine masu amfani, Folwoya Goriji, wani gari a jihar Adamawa, na fuskantar kangin rayuwa - A garin babu tsaftataccen ruwan sha wanda hakan yasa mazauna garin ke shan ruwa a kogi daya da dabbobinsu 


Mazauna yankin, yayinda suke korafi, sun bukaci a kawo masu dauki saboda suna tunanin an manta da su Folwoya Goriji, wani garin manoma a yankin Ndikong da ke karamar hukumar Mayo Belwa na jihar Adamawa, na da hanyar samun ruwa guda daya ne tal. 



Abun bakin ciki, a wuri guda mutane da dabbobi ke samun ruwan sha. A cewar The Pilot, wannan garin sun dogara ne a kan ruwan kogo wajen gudanar da harkokinsu na yau da kullun, sannan sun yarda cewa wakilan jiharsu da na hukumarsu sun watsar da su. 


Al’umman kauyen na rokon gwamnatocin jiha da na kananan hukumomi su share masu hawayensu daga illar da ke tattare da shan ruwa a waje guda da dabbobinsu. 


An kawo Baba Musa, wani mazaunin kauyen, ya na fadin cewa: “A lokacin yakin neman zabe ne kawai muke ganinsu (yan siyasa) tare da alkawaransu na bogi da karya. Don Allah, kalli ruwan da muke sha tare da dabbobinmu kamar an manta da mu. 


“Dan Allah ku fada masu kokenmu,” yan asalin garin.” Da yake martani ga koken Musa, wani mai kare hakkin dan adam, Ibrahim Makejo, ya bayyana cewa ba garin kadai bane domin akwai saura da ke fuskantar irin wannan wahala ta rayuwa. 


Ya ce: “Ruwan sha mai inganci, gyara da tsafta na daga cikin hanyoyi biyar na dakile cututtuka. “Saboda haka yana da muhimmanci zababbun shugabanninmu su samar da ruwa mai inganci, da tabbatar da tsaftar muhalli da na jiki a yankunan karkara.


Legit.ng ta yi kokarin samun kansila da ke wakiltan yankin amma abun ya ci tura domin an ce baya gari. Yunkurin jin ta bakin Shugaban karamar hukumar ma bai haifar da yaya masu idanu ba. 



SOURCE: LEGIT


Mtn Data Bonanza By Bz Global Services 🌐

1GB @N350 

2GB @N700

3GB @N1,050

4GB @N1,400

5GB @N1,750

Validity For 30Days

Hanyar Biya Bank Transfer Domin Siya Yanzu Kiramu Ta Number Waya 08133888333 Koka Aiko Sako Ta Whatsapp: 09066633320


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765


Related Posts

0 Response to "Kalli Hotunan wani Yanki A jihar Adamawa inda jama'a ke shan ruwa daya da dabbobinsu "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?