--
Gazawar shugaban kasa wurin bada tsaro abu ne da zai sa tsigesa, Osinbajo a 2015

Gazawar shugaban kasa wurin bada tsaro abu ne da zai sa tsigesa, Osinbajo a 2015



Sakamakon kashe-kashen da 'yan Boko Haram suke yi a Najeriya, mutane sun yi wani waiwaye adon tafi - 'Yan Najeriya sun tunatar da mataimakin shugaban kasa, Osinbajo wata wallafa da yayi a Twitter a 2015 lokacin yana kamfen 


A ranar 8 ga watan Fabrairun 2015 ne Osinbajo yace in dai Jonathan bai iya kare rayukan al'umma ba, ya cancanci a tsige shi Sakamakon kashe-kashen da 'yan Boko Haram suke tayi a Najeriya, 'yan Najeriya sun tunatar da mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo a kan wata wallafarsa da yayi a 2015 a shafinsa na kafar sada zumuntar zamani ta Twitter. 


Lokacin da Osinbajo yake kamfen a 2015, ya wallafa; "Idan shugaban kasa yace ba zai iya kulawa da rayuka da kuma dukiyoyin al'umma ba, tabbas laifi ne da yayi wanda ya cancanci a tsigeshi." 


Ya yi wannan wallafar ne a ranar 8 ga watan Fabrairun 2015, wanda mutane suka yi ta tsokaci suna yabonsa. A ranar Asabar, mayakan Boko Haram sun kashe fiye da mutane 43 a wata gonar shinkafa da ke kusa da Maiduguri jihar Borno, Vanguard ta wallafa. 


Kamar yadda AFP ta ruwaito, Boko Haram da ISWAP sun fara kai wa manoma, makiyaya da masunta hari, inda suke zarginsu da leken asiri da sanar da labaransu ga sojojin Najeriya, shiyasa sojojin suke kai musu farmaki. 


A watan da ya gabata, AFP ta ruwaito yadda 'yan Boko Haram suka yi wa wasu manoma 22 yankan rago suna tsaka da noman rani a kusa da Maiduguri a hare-hare 2 daban-daban. Ministan labarai da al'adu, Alhaji Lai Mohammad, ya ce yanzu haka Najeriya tana hannun 'yan ta'adda suna yadda suka ga dama saboda an hana Najeriya makamai don yakar 'yan ta'adda. 



SOURCE: LEGIT

Mtn Data Bonanza By Bz Global Services 🌐

1GB @N350 

2GB @N700

3GB @N1,050

4GB @N1,400

5GB @N1,750

Validity For 30Days

Hanyar Biya Bank Transfer Domin Siya Yanzu Kiramu Ta Number Waya 08133888333 Koka Aiko Sako Ta Whatsapp: 09066633320


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

Related Posts

0 Response to "Gazawar shugaban kasa wurin bada tsaro abu ne da zai sa tsigesa, Osinbajo a 2015"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?