--
Gagarumin rikici ya barke bayan 'yan daba sun fada kotu tare da fatattakar alkali da lauyoyi

Gagarumin rikici ya barke bayan 'yan daba sun fada kotu tare da fatattakar alkali da lauyoyi


An tsananta tsaro a harabar babbar kotun tarayya da ke Yenagoa saboda gudun 'yan ta'adda - A ranar Alhamis da ta gabata ne 'yan ta'adda dauke da makamai suka afka wa kotun, inda suka fatattaki lauyoyi 


Sun yi kaca-kaca da duk wasu takardu da abubuwan amfanin kotun, sun kuma sace kudade da wayoyi An tsananta tsaro a harabar babbar kotun tarayya da ke Yenagoa, jihar Bayelsa a ranar Juma'a don gudun kutsawar 'yan ta'adda kamar yadda suka yi a ranar Alhamis da rana.


'Yan ta'addan da ke dauke da miyagun makamai, wadanda yawansu ya kai 20, inda suka fi karfin jami'an tsaro kuma suka kutsa cikin kotu mai daraja ta II, wacce take kula da tsayar da 'yan takarar jam'iyyar APC da na PDP a Bayelsa ta tsakiya. 


Sun lalata duk wasu abubuwa masu muhimmanci na ofishin da ake ajiye kayan shari'ar da kuma kayan amfanin kotun, Vanguard ta wallafa. 'Yan ta'addan sun fatattaki lauyoyi da ma'aikatan kotun, sannan sun kwashe kudade, wayoyi da sauran abubuwa masu daraja. 


SOURCE: LEGIT


Mtn Data Bonanza By Bz Global Services 🌐

1GB @N350 

2GB @N700

3GB @N1,050

4GB @N1,400

5GB @N1,750

Validity For 30Days

Hanyar Biya Bank Transfer Domin Siya Yanzu Kiramu Ta Number Waya 08133888333 Koka Aiko Sako Ta Whatsapp: 09066633320


LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "Gagarumin rikici ya barke bayan 'yan daba sun fada kotu tare da fatattakar alkali da lauyoyi "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?