
Kaico: Wani mutum ya sare kan wani magidanci da ɗansa a Kano
Wani mutum ya sare kan wani magidanci tare da sassara ɗansa a ƙauyen Tumfafi na Ƙaramar Hukumar Garko da ke Jihar Kanon Najeriya.
Mutumin wanda har yanzu ba a kai ga gano ko wane ne ba, ya kutsa gidan Malam Nuhu Muhammad a daren jiya Lahadi sannan ya fille masa kai da adda.
Bayanan da wakilin BBC a Kano Zahraddeen Lawan ya tattaro sun nuna cewa lamarin ya faru ne kafin maƙwabta su ankara da abin da ke faruwa a cikin daren.
"Da misalin ƙarfe 2:00 na dare sai mahaifimmu ya tashe mu yake faɗa mana abin da ke faruwa, da ɗansa ya bi sahu domin ganin abin da ya faru da mahaifinsa sai shi ma mutumin ya sare shi a ka da hannu kuma ya kashe shi," a cewar wani maƙwabcin marigayin.
Ya ƙara da cewa ita ma matar marigayin da ƙyar ta tsallake bayan da maharin ya kai mata sara bai same ta ba.
Ga alama dai da ma akwai wata jiƙaƙƙiya tsakanin maharin da mamacin, kodayake kawo yanzu babu wani cikakken bayanin abin da ke tsakaninsu a hukumance.
SOURCE: BBCHAUSA
0 Response to "Kaico: Wani mutum ya sare kan wani magidanci da ɗansa a Kano"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?