--
A raba ni da shi, gagarumin mashayi ne kuma yana dukana - Matar aure ga kotu

A raba ni da shi, gagarumin mashayi ne kuma yana dukana - Matar aure ga kotu


Wata Munirat Obaro, ta roki kotu ta raba aurensu da mijinta Abdullaziz Mohammed - Ta ce mijin nata yana shaye-shaye, yana kuma dukanta har da yunkurin kasheta - Alkalin ya ce bata kawo gamsassun hujjoji ba, 


don haka yaki raba auren Wata matar aure mai suna Munirat Obaro, ta roki wata kotu da ke zama a Gwagwalada ta raba aurenta na shekara 17 da mijinta, Abdullaziz Mohammed, wanda ta ke zarginsa da shaye-shaye. Munirat, mai yara 4, 


wacce take zaune a Anguwar Shani, ta zargi mijinta da dukanta akai-akai har da yunkurin kasheta. Mohammed ya musanta zargin da take yi masa, inda yace "Matata tayi min kazafi, duk da a shirye nake da na canja duk halayena wadanda bata so."


Alkali mai shari'ar, Adamu Isah, ya ce shaidun da ta gabatar a gaban kotu basu da karfi don haka kotu ta ki amincewa da raba auren. Yace su cigaba da zama a matsayin mata da miji, Daily Trust ta wallafa.


SOURCE: LEGIT.NG

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "A raba ni da shi, gagarumin mashayi ne kuma yana dukana - Matar aure ga kotu "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?