--
WAEC Za Ta Fitar Da Sakamakon SSCE Na 2020 A Makon Gobe

WAEC Za Ta Fitar Da Sakamakon SSCE Na 2020 A Makon Gobe


Hukumar Shirya Jarabawa ta Yammacin Afirkta (WAEC) ta dage ranar fitar da sakamakon jarabawarta na kammala sakandare da aka gudanar bana zuwa mako mai zuwa.


A ranar Laraba 28 ga Oktoboa ya kamata WAEC ta fitar da sakamakon jarabawar amma ta ce ta dage saboda rikici da kone-konen da aka yi a boren #EndSARS a sassan Najeriya.


“A yau Hukumar ta shirya fitar da sakamakon jarabawar amma dokar hana fita da aka sanya a makon jiya ya sa aka dage fitar da sakamakon zuwa makon gobe. Nan gaba za a sanar da ainihin ranar”, inji sanarwar da WAEC ta wallafa a shafinta na Twitter.


Jami’in Hulda ja Jama’a na Ofishin Hukumar a Najeriya, Demianus Ojijeogu, ya tabbatar da hakan.


Idan ba a manta ba bullar annobar COVID-19 da dokar kulle da aka sanya domin dakile yaduwarta ta sanya an daga gudanar da jarabawar a Najeriya da wasu kasashe.


A baya an saba gudanar da jarabawar ne tsakanin watan Mayu da Yuni, amma bullar a annobar ta sa a 2020 aka gudanar a watan Agusta.


Source: Aminiya Daily Trust

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:

LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:


KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: 

KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA 
@FACEBOOK:

@TWITTER: 

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765

0 Response to "WAEC Za Ta Fitar Da Sakamakon SSCE Na 2020 A Makon Gobe"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?