SARS: Sufeton ƴan sandan Najeriya ya haramta wa rundunar kafa shingayen bincike
Sufeto Janar na ƴan sandan Najeriya Mohammed Adamu ya haramta wa runduna ta musamman mai yaƙi da fashi da makami da ake kira SARS da sauran ɓangarorin rudunonin ƴan sanda kafa shingayen bincike.
Cikin sanarwar da shafin Twitter na rundunar ƴan sandan Najeriya ya wallafa a wasu jerin saƙwanni ranar Lahadi, sufeton ƴan sandan ya haramta wa dukkanin rundunoni na musamman da suka haɗa da FSARS da STS da IRT da ke yaƙi da ƙungiyoyin asiri kafa shingayen bincike domin tarewa da binciken ababen hawa.
Sannan an haramta wa duk wani jami'in ƴan sanda fitowa da kayan gida ba tare da kayan ƴan sanda ba. Sanarwar ta ce wasu jami'an na fakewa da wannan suna yin abubuwan da ba su dace ba da suka saɓa doka.
Babban Sufeton ƴan sandan ya kuma yi gargaɗi ga rundunonin game shiga haƙƙin sirrin rayuwar mutane musamman bincike wayoyinsu na salula da kwanfuta da sauran na'urori ba tare da wani samun izini ba.
Sanarwar ta ce an kama wasu daga cikin jami'an SARS da ake zargi da cin zarafin mutane a Legas, sannan za a ci gaba da bincike kan zargin cin zarafi da wasu jami'an rundunar SARS suka aikata.
An buƙaci jami'an su mayar da hankali ga laifukan da suka shafi fashi da makami da satar mutane da sauran muggan laifukan da aka kafa rundunonin domin su, ba su koma cin zarafin al'umma ba.
Kauce wa Twitter, 1
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1
Dubban 'yan Najeriya ne suka hau shafukan sada zumunta tun daga daren Asabar domin nuna bacin ransu da kuma yin kiran da a kawo ƙarshen ayyukan rundunar, inda suka riƙa amfani da maudu'ai irinsu #EndSARS #EndSarsSNow #EndPoliceBrutality.
Dukkanin maudu'an uku na cikin waɗanda aka fi tattaunawa a kansu a dandalin Twitter.
Wannan matakin da rundunar ƴan sandan Najeriya ta ɗauka ya biyo bayan bidiyo da dama da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke nuna yadda jami'an rundunar ta SARS ke cin zarafin mutane ta hanyar ƙarbar kuɗi har ma da harbin mutane.
Ɗaya daga cikin bidiyon da ke yawo a kafofin sadarwa na intanet ya nuna yadda aka cacumi wani mutum da aka jefa a mota aka tafi da shi.
Tun da farko gwamnatin Jihar Legas ta ce za ta ɗauki mataki kan jami'an rundunar ta musamman mai yaƙi da fashi da makami da ta SARS.
Kauce wa Twitter, 2
Karshen labarin da aka sa a Twitter, 2
"Rahotannin yin ƙwace daga mutanen da aka ɗauka domin su kare al'umma abu ne mai tayar da hankali," in ji Gwamna Sanwo-Olu a wani saƙon Twitter.
"Ina tabbatar muku cewa za a ɗauki matakin da ya dace kuma cikin gaggawa."
Tuni da ma ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta yi kiran da a soke ayyukan rundunar sakamakon kisan babu gaira ba dalili da azabtar da waɗanda ake zargi da laifi.
Duk da cewa Gwamna Sanwo-Olu ya yi alƙawarin ɗaukar mataki, sai dai rundunar tana aiki ne a ƙarƙashin Gwamnatin Tarayyar Najeriya, abin da ke nuna cewa babu tabbaci kan irin matakin da gwamnan zai ɗauka.
Babban sufeton ƴan sandan Najeriya ya jaddada ƙudirinsa ga ƴan Najeriya na gyara ayyukan rundunar ƴan sanda wacce za ta kasance mai aiki da kare ƴancin ƴan kasa da kuma kiyaye haƙƙokin da tabbatar da tsaron al'umma.
Ya yi kira ga ƴan Najeriya kada su bari ɗabiun wasu tsirarun jami'an ƴan sandan su tasiri ga imani da amince da suke da shi ga rundunar ƴan sanda.
other Tactical Squads of the Force including the Special Tactical Squad (STS), Intelligence Response Team (IRT), Anti-Cultism Squad and other Tactical Squads operating at the Federal, Zonal and Command levels, from carrying out routine patrols and other conventional low-risk
— Nigeria Police Force (@PoliceNG) October 4, 2020
They must always appear in their police uniforms or approved tactical gear. The IGP’s directives come against the backdrop of findings by the leadership of the Force that a few personnel of the Tactical Squads hide under these guise to perpetrate all forms of illegality,
— Nigeria Police Force (@PoliceNG) October 4, 2020
search of mobile phones, laptops and other smart devices. They are to concentrate and respond only to cases of armed robbery, kidnapping and other violent crimes when the need arises.
— Nigeria Police Force (@PoliceNG) October 4, 2020
Dubban 'yan Najeriya ne suka hau shafukan sada zumunta tun daga daren Asabar domin nuna bacin ransu da kuma yin kiran da a kawo ƙarshen ayyukan rundunar, inda suka riƙa amfani da maudu'ai irinsu #EndSARS #EndSarsSNow #EndPoliceBrutality.
Dukkanin maudu'an uku na cikin waɗanda aka fi tattaunawa a kansu a dandalin Twitter.
Wannan matakin da rundunar ƴan sandan Najeriya ta ɗauka ya biyo bayan bidiyo da dama da ke yawo a shafukan sada zumunta da ke nuna yadda jami'an rundunar ta SARS ke cin zarafin mutane ta hanyar ƙarbar kuɗi har ma da harbin mutane.
Ɗaya daga cikin bidiyon da ke yawo a kafofin sadarwa na intanet ya nuna yadda aka cacumi wani mutum da aka jefa a mota aka tafi da shi.
Tun da farko gwamnatin Jihar Legas ta ce za ta ɗauki mataki kan jami'an rundunar ta musamman mai yaƙi da fashi da makami da ta SARS.
The safety of our residents is my number one duty as the CSO of Lagos. So, reading reports of seemingly unlawful exploitation by the people charged to protect is very worrying & needs to be addressed immediately. Be assured that appropriate actions will be taken, & speedily too.
— Babajide Sanwo-Olu (@jidesanwoolu) October 4, 2020
"Rahotannin yin ƙwace daga mutanen da aka ɗauka domin su kare al'umma abu ne mai tayar da hankali," in ji Gwamna Sanwo-Olu a wani saƙon Twitter.
"Ina tabbatar muku cewa za a ɗauki matakin da ya dace kuma cikin gaggawa."
Tuni da ma ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta yi kiran da a soke ayyukan rundunar sakamakon kisan babu gaira ba dalili da azabtar da waɗanda ake zargi da laifi.
Duk da cewa Gwamna Sanwo-Olu ya yi alƙawarin ɗaukar mataki, sai dai rundunar tana aiki ne a ƙarƙashin Gwamnatin Tarayyar Najeriya, abin da ke nuna cewa babu tabbaci kan irin matakin da gwamnan zai ɗauka.
Babban sufeton ƴan sandan Najeriya ya jaddada ƙudirinsa ga ƴan Najeriya na gyara ayyukan rundunar ƴan sanda wacce za ta kasance mai aiki da kare ƴancin ƴan kasa da kuma kiyaye haƙƙokin da tabbatar da tsaron al'umma.
Ya yi kira ga ƴan Najeriya kada su bari ɗabiun wasu tsirarun jami'an ƴan sandan su tasiri ga imani da amince da suke da shi ga rundunar ƴan sanda.
Source: Legit.ng
0 Response to "SARS: Sufeton ƴan sandan Najeriya ya haramta wa rundunar kafa shingayen bincike"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?