
#EndSARS: El-Rufa’i Ya Kara Fadada Dokar Hana Fita A Kaduna
Sunday, 25 October 2020
Comment
Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 da za ta game jihar baki daya sabanin sanarwar farko da ta takaita a wasu kananan hukumomin jihar biyu da suka hada da Chikun da Kaduna ta Kudu, inda a yanzu dokar ta game baki daya kananan hukumomi 23 da ke jihar.
Jawabin ya fito ta bakin Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin gida, Samuel Aruwan a daren Asabar, ya kuma ce dokar zaman gidan ta gama-gari za ta fara aiki nan take.
Gwamnatin jihar ta ce ta dauki wannan matakin saboda da kare lafiya da dukiyoyin al’umma da dakile shirin bata-gari na satar kayayyakin gwamnati.
Kwamishinan ya bukaci jama’ar jihar Kaduna da su zama ‘yan kasa jakadu nagari, kuma su bawa gwamnatin jihar dukkan hadin kai da goyan baya su kuma kiyaye doka da oda da bin umarnin gwamnati kamar yadda aka bukata.
Source: Aminiya Daily Trust
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A WHATSAPP:
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI A TELEGRAM:
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN:
KU BIYOMU A SHAFUKAN SADA ZUMUNTA NA
@FACEBOOK:
@TWITTER:
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app75765
0 Response to "#EndSARS: El-Rufa’i Ya Kara Fadada Dokar Hana Fita A Kaduna"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?