
Femi Falana SAN ya sa an karbo takardu, zai daukaka kara a shari’ar Aminu Shariff
Thursday, 3 September 2020
Comment
Ana kokarin daukaka karar Yahaya Aminu Shariff zuwa gaban babban kotu - Kotu ta samu Yahaya Aminu Shariff da laifin cin mutuncin musulunci a baya
Wannan ya sa Alkalin karamin kotun shari’a ya yanke masa hukuncin kisa Ana kishin-kishin din cewa shahararren lauyan nan, Femi Fakana SAN, zai tsayawa Yahaya Aminu Shariff wanda aka yankewa hukucin kisan-kai.
Babban Lauyan zai kare wannan matashi mai shekaru 22 da haihuwa da Alkali ya samu da laifin cin mutuncin addinin musulunci a jihar Kano kwanakin baya. Rahotannin da su ke zuwa mana a ranar Alhamis, 3 ga watan Satumba, 2020, sun bayyana cewa Femi Falana ya samu karbar takardun.
wannan shari’a da ake yi. Hakan na zuwa ne makonni uku da samun Aminu Shariff da laifi a gaban wani kotun shari’a. Falana zai tsaya wajen ganin an daukaka kara domin a saki matashin.
Mai magana da yawun bakin bangaren shari’a na jihar Kano, Babajido Ibrahim, ya sanar da manema labarai wannan cigaba da aka samu a shari'ar dazu da rana.
Mista Babajido Ibrahim ya ce takardun wannan kara da zaman kotun da aka yi sun kai ga Femi Falana, a madadin wani Lauya da ya aiko ya wakilce sa a jihar Kano. An gabatarwa wakilin Femi Falana SAN wadannan takardu ne a ranar 2 ga watan Satumba.
Wannan zai bada damar lauyan ya kare wanda ake tuhuma a gaban kuliya. Falana wanda ya yi fice wajen kare hakkin Bil Adama, zai duba hukuncin da Alkalin kotu ya yanke a watan Agusta, daga nan ya garzaya kotu, ya daukaka wannan shari’a.
Wannan shari’a ta jawo ce-ce-ku-ce har a ketare, inda wasu su ke ganin bai kamata a yankewa mutum hukuncin kisa a kasar da kowa ya ke da ‘yancin yin magana ba. A gefe guda, masana addinin musulunci sun yaba da hukuncin da Khadi Aliyu Muhammad na kotun shari’a da ke Hausawa ya yi, sun ce haka addinin musulunci ya tanada.
SOURCE: Legit.ng
DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
SAYI KWAKWKWARAR DATAR MTN MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN:
https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A SHAFUKAN
@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
Wannan ya sa Alkalin karamin kotun shari’a ya yanke masa hukuncin kisa Ana kishin-kishin din cewa shahararren lauyan nan, Femi Fakana SAN, zai tsayawa Yahaya Aminu Shariff wanda aka yankewa hukucin kisan-kai.
Babban Lauyan zai kare wannan matashi mai shekaru 22 da haihuwa da Alkali ya samu da laifin cin mutuncin addinin musulunci a jihar Kano kwanakin baya. Rahotannin da su ke zuwa mana a ranar Alhamis, 3 ga watan Satumba, 2020, sun bayyana cewa Femi Falana ya samu karbar takardun.
wannan shari’a da ake yi. Hakan na zuwa ne makonni uku da samun Aminu Shariff da laifi a gaban wani kotun shari’a. Falana zai tsaya wajen ganin an daukaka kara domin a saki matashin.
Mai magana da yawun bakin bangaren shari’a na jihar Kano, Babajido Ibrahim, ya sanar da manema labarai wannan cigaba da aka samu a shari'ar dazu da rana.
Mista Babajido Ibrahim ya ce takardun wannan kara da zaman kotun da aka yi sun kai ga Femi Falana, a madadin wani Lauya da ya aiko ya wakilce sa a jihar Kano. An gabatarwa wakilin Femi Falana SAN wadannan takardu ne a ranar 2 ga watan Satumba.
Wannan zai bada damar lauyan ya kare wanda ake tuhuma a gaban kuliya. Falana wanda ya yi fice wajen kare hakkin Bil Adama, zai duba hukuncin da Alkalin kotu ya yanke a watan Agusta, daga nan ya garzaya kotu, ya daukaka wannan shari’a.
Wannan shari’a ta jawo ce-ce-ku-ce har a ketare, inda wasu su ke ganin bai kamata a yankewa mutum hukuncin kisa a kasar da kowa ya ke da ‘yancin yin magana ba. A gefe guda, masana addinin musulunci sun yaba da hukuncin da Khadi Aliyu Muhammad na kotun shari’a da ke Hausawa ya yi, sun ce haka addinin musulunci ya tanada.
SOURCE: Legit.ng
DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
SAYI KWAKWKWARAR DATAR MTN MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN:
https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A SHAFUKAN
@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Femi Falana SAN ya sa an karbo takardu, zai daukaka kara a shari’ar Aminu Shariff "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?