
Yanzu-yanzu: Farfesa Sagir Adamu na gab da zama shugaban jami'ar Bayero Kano, ya doke sauran yan takaran a zabe
Wednesday, 5 August 2020
Comment
Daily Trust ta tattaro cewa wannan zaben na al'ummar jami'ar na da muhimmanci wajen sanin wanda zai zama shugaban jami'ar.
Ana kyautata zaton za'a gudanar da matakin zaben na karshe ranar Asabar, inda yan takaran zasu gurfana gaban kwamitin zabe.
Amma, an tattaro cewa, bisa al'adar jam'iar, duk wanda ya lashe zaben nan da Farfesa Sagir ya lashe, ke zama shugaban jami'ar.
Farfesa Sagir masanin ilimin lissafi ne, kuma ya fara rayuwarsa a jami'ar matsayin mataimakin lakcara a 1991 har ya zama farfesa. A baya ya rike kujerar diraktan sashen bincike kuma daga bisani mataimakin shugaban jami'ar (sashen harkokin karatu) a jami'ar.
A shekarar 2013, an nada shi babban hadimin tsohuwar ministar Ilimi, Farfesa Ruqayyatu Rufa'i. Sauran yan takaran sune Farfesa Mohammed Dikko Aliyu daga jami'ar King Fahad, Saudi Arabia wanda ya samu kuri'u 10 da Farfesa Dalhatu Balarabe Yahaya wanda ya samu kuri'u biyar.
SOURCE: LEGIT.NG
DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Yanzu-yanzu: Farfesa Sagir Adamu na gab da zama shugaban jami'ar Bayero Kano, ya doke sauran yan takaran a zabe"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?