
Kotu ta daure mai walda saboda sata
Dan sanda mai gabatar da kara, Sifeto Adeoye Kayode ya fada kotu cewar da misalin 11:20 na daren ranar 18 ga watan Agusta, 2020, mai laifin ya yi aika aikan a titin Basi Bankole da ke Oke Onitea, a Osogbo.
Adwoye ya ce mutumin ya fasa shagon wani da ake kira Azeez Fatai, ya sace kan fankar sama, man mota, dutsin guga biyu lalatattu da koyal da kuma fankar kasa da darajarsu ta kai N60,000.
Ya ce, laifin da ya saba doka kuma za a hukunta shi karkashin sashe na 413 da 309 na dokar manyan laifuka ta Jihar Osun ta 2002.
Mai laifin, Kola Rasheed, wanda bai dauki lauyan da zai kare shi ba, bai musunta zargin da aka yi masa ba.
Sai dai ya ce makwabta sun doke shi suka kuma sace masa N2,500 da ke aljihusa kafin isowar ‘yan sanda.
A hukuncin da ya yanke, Mai Shari’a Opeyemi Badmus, ya tura mai laifin gidan yari na wata shida ba tare da zabin tara ba.
SOURCE: AMINIYA DAILY TRUST
DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
SAYI KWAKWKWARAR DATAR MTN MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN:
https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A SHAFUKAN
@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657757657
0 Response to "Kotu ta daure mai walda saboda sata"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?