
Jihar da yara miliyan biyu ba sa zuwa makaranta
Hakan ta sa gwamnatin jihar bullo da shirin sanya ilimin boko a tsarin makarantun allo da kuma ciyar da almajirai a makarantun.
Manufar shirin ita ce, ”Ba wa wadannan yara damar lakantar ilimin dukkanin bangarorin biyu, da kuma dakile matsalar barace-barace”, a cewar hukumar ilimin bai daya ta jihar.
Shugaban hukumar Abubakar Aliyu Maradun ya kara da cewa za a fara shirin ne yara 30,000 a makarantu 280 daga a kananan hukumomi takwas.
Ya ce ”An tanadi kayayyakin karatu, littattafan yara da kuma malaman, sannan muna ba su abinci sau daya a kullum”.
Jihar ta gano girmar matsalar yaran marasa zuwa makaranta ne bayan alkaluman da a baya suka nuna cewa yara miliyan daya ne a jihar ba sa zuwa makaranta.
Zamfara na daga jihohin da matsalar tsaro ta yi kamari, sakamakon hare-haren ’yan bindiga.
Ayyukan bindiga a jihar sun yi sanadiyar mutuwar mutane da dama baya ga tilasta wa dubbai tserewa daga gidajensu.
SOURCE: LEGIT.NG
DAGA: BZGLOBALSERVICE.COM.NG
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARAI TA WHATSAPP:
https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
SAYI KWAKWKWARAR DATAR MTN MAI KYAU DA INGANCI ANAN DOMIN SIYA YANZU LATSA NAN↓↓↓
https://paystack.com/pay/mz-st-fdub
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN:
https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A SHAFUKAN
@FACEBOOK: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
@TWITTER: https://twitter.com/bzglobalsevice
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Jihar da yara miliyan biyu ba sa zuwa makaranta"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?