Yanzu-yanzu: Gwamna Wike ya kwaci matar da ta zargi Akpabio da neman jima'i da ita bayan yan sanda sun yiwa gidanta zobe
Thursday, 16 July 2020
Comment
Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya kwace tsohuwar MD na hukumar cigaban yankin Neja Delta NNDC, Joi Nunieh,
bayan an garkameta cikin gidanta dake Port Harcourt, babbar birnin jihar. Bidiyon TVCNews ya nuna yadda gwamnan ya shiga cikin gidan kuma ya umurci yan sandan su fice sannan ya tafi da ita.
#NDDCSAGA: Rivers state governor, Nyesom Wike rescues former NDDC MD, Joy Nunieh from "house arrest."— TVC News (@tvcnewsng) July 16, 2020
Governor Wike forced entry into Joy Nunieh's residence, ordered police officers out and later drove off with her. pic.twitter.com/qJmaUm5Cba
Mun kawo muku rahoton cewa Jami'an 'yan sandan Najeriya sun tsinkayi gidan Joy Nunieh, tsohuwar mukaddashin manajan daraktan hukumar habaka yankin Neja Delta (NDDC), inda suka yi masa zobe.#NDDCSAGA: Rivers state governor, Nyesom Wike rescues former NDDC MD, Joy Nunieh from "house arrest."— TVC News (@tvcnewsng) July 16, 2020
Governor Wike forced entry into Joy Nunieh's residence, ordered police officers out and later drove off with her. pic.twitter.com/zT72Eh7ftH
Jami'an tsaron sun isa gidan ne da ke lamba 3, titin Owuru Creek, kusa da titin Herbert Macauley da ke tsohuwar GRA a Fatakwal, jihar Ribas a sa'o;in farko na ranar Alhamis. Wannan ya faru ne kafin isar Nunieh gaban kwamitin bincike na majalisar dattawa da ke Abuja inda za ta amsa tambayoyi a kan ayyukan NDDC.
A yayin da jaridar The Cable ta yi kokarin jin ta bakin kakakin rundunar 'yan sandan jihar Ribas, Omoni Nnamdi don tsokaci, ya bukaci a kira sa nan da mintuna 30. Nunieh, a wata tattaunawa da aka yi da ita a baya bayan nan, ta zargi ministan da cin hanci da rashawa, cin zarafi da kuma muzgunawa ma'aikata, fasa bututun mai,
shiga cikin ayyuka kungiyoyin asiri, karya dokokin aikinsa da sauransu. Hakazalika ta zargeshi da kokarin taba mata jiki da kwaciya da ita amma ta waska masa mari a cikin gidansa dake unguwar Apo dake birnin tarayya Abuja. Amma Ministan na gaban yankin Niger Delta, Godswill Akpabio, ya karyata zarginsa da Ms. Gbene Joi Nuneih, na cewar ya yi kokarin zina da ita.
Ministan, a cikin wata sanarwa da ya bayar a ranar Laraba a Abuja ta hannun Aietie Ekong, hadiminsa ta fuskar watsa labarai, ya ce wannan zargin da ta yi wasa, "karyace kawai tsagoronta". "Duk kalamanta karairayi ne kawai, babu gaskiya a ciki.
"Ministan bai aikata ba, ko a wani waje, ko a wani lokaci, ko a cikin wani hali, bai ci zarafin Ms. Nunieh, balle ma har ace ya yi yunkurin kamanta wani abu da ya shafi fyade ga Ms. Nunieh, ko kuma wata mace a cikin ma'aikatar ko hukumar NDDC," a cewar sanarwar.
SOURCE: LEGIT.NG
TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Yanzu-yanzu: Gwamna Wike ya kwaci matar da ta zargi Akpabio da neman jima'i da ita bayan yan sanda sun yiwa gidanta zobe"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?