
Yanda Wani soja ya harbe kwamandansa a Borno
Thursday, 30 July 2020
Comment
Wani kurtun soja ya hallaka kwamandansa bayan ya yi masa ruwan harsasai a yankin Bama na Jihar Borno.
Sojan ya harbe Laftanar Babakaka Ngirgi sau takwas, al’amarin da ya yi sanadiyar mutuwar hafsan a ranar Laraba.
Majiyarmu ta soji ta ce kurtun wanda yanzu yake tsare ya dade yana kullatar hafsan wanda suke aiki tare a Bataliyar Tankoki ta 202 a Karamar Hukumar Bama ta Jihar Borno.
Ta ce kurtun ya bude wa mamacin wuta ne ta baya kuma a kusa da shi, inda nan take ya rasu.
A ranar Alhamis za a yi jana’izar Laftanar Babakaka Ngorgi a barikin sojan kasa na Maimalari da ke Maiduguri.
Majiyar ta ce a ‘yan shekarun an samu irin wannan matsalar tsakanin sojoji rundunar Operation Lafiya Dole mai yaki da Boko Haram a Gwoza, Chibok, Bama da kuma Mallam Fantori.
Mamacin ya kammala kwalejin kananan hafsoshi ta NDA ne a 2016, sannan ya yi aure watan Disamban 2019.
SOURCE:https://aminiya.dailytrust.com.ng/
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Yanda Wani soja ya harbe kwamandansa a Borno"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?