--
Tirkashi: 'Yar shekara 12 ta auri mutum biyu a wata ɗaya

Tirkashi: 'Yar shekara 12 ta auri mutum biyu a wata ɗaya




‘Yan sanda a Kenya sun ceto wata yarinya mai shekara 12 da aka aurar da ita ga maza biyu cikin wata ɗaya.

Mahaifin yarinyar da ke zaune a garin Narok na yammacin babban birnin ƙasar Nairobi, shi ne ya tilasta mata auren wani mutum mai shekara 51.

Bayan ta gudu ne kuma aka sake aurar da ita ga wani mai shekara 35 kafin daga bisani wasu masu fafutikar kare haƙƙi da jami’an gwamnati su ceto ta.

Aurar da ‘yan ƙasa da shekara 18 laifi ne a Kenya.

Wani mai kare haƙƙi ya ce ya samu labarin yarinyar ne yayin da yake tsaka da ceto wata yarinyar daban.

“Mahaifinta ya bayar da ita ga wani dattijo.

Ba ta da wani zaɓi illa ta auri wanda bai kai shi tsufa ba,” in ji Joshua Kaputah na ƙungiyar the Narok County Peace Association.

SOURCE: BBCHAUSA

TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Tirkashi: 'Yar shekara 12 ta auri mutum biyu a wata ɗaya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?