--
Da Dumi duminsa: Za a koma makarantun Islamiya a Kano

Da Dumi duminsa: Za a koma makarantun Islamiya a Kano


Gwamnan Kano; Abdullahi Umar Ganduje Hakkin mallakar hoto; Fadar Gwamnatin Kano


Mun samu rahoton cewa, ana daf da buɗe makarantun Islamiya a jihar Kano kamar yadda Gidan Rediyon Freedom ya ruwaito.

Hukumar makarantun Islamiya ta jihar ta bukaci malamai iyaye da kuma ɗaliban makarantu da su ci gaba da daukan dangana a yayin da saura ƙiris a buɗe makarantun baki ɗaya.

Hukumar ta sanar da cewa nan ba daɗewa za a buɗe makarantu a yayin da gwamnatin jihar ta ke ci gaba da tattaunawa hukumomin lafiya bisa la'akari da annobar korona.

Shugaban hukumar, Sheikh Gwani Yahuza Gwani 'Dan Zarga, shi ne ya fayyace hakan a wata hira da ya yi da manema labarai.

Gwani Yahuza ya bayyana damuwar da gwamnatin jihar ta yi dangane da yadda ɗalibai ke ci gaba da zaman dirshan a gidan babu karatun Arabi bare na Boko sakamakon annobar korona.
Malamin sha kundum a ilimin Al-Qur'ani, ya ce tabbas annoba gaskiya ce kuma addinin Islama ya koyar daukan duk wasu matakan kariya yayin da ta bulla a cikin al'umma.

Ana iya tuna cewa tun a watan Maris ne gwamnatin Najeriya ta bada umarnin rufe kafatanin makarantun kasar manya da kanana a matsayin matakin dakile yaduwar cutar korona wadda ta bulla karo na farko a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Legit.ng ta kuma ruwaito cewa, gwamnatin tarayya ta ce Najeriya zata fuskanci wata babbar annoba ma damar ta kasa amfani da yanayin da annobar korona wajen bunkasa fannin kiwon lafiya.

Sakataren gwamnatin tarayya (SGF) Mr Boss Mustapha ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da hukumar kwararru (BoE) na shirin bincike da bunkasa kiwon lafiya (HSRDIS) a Abuja.

A cewar sa: "Idan har muka tsallake wannan yanayin, to lallai zamu fuskanci wata annobar kuma ba zamu iya tsinana komai ba.

"Idan da ace mun bunkasa fannin kiwon lafiya a lokacin annobar Ebola, da bamu sha wahalar da muka sha a yanzu ba, tunda cibiyoyin gwajin COVID-19 biyu kadai garemu."

Ya kara da cewa: "Idan da zaka zagaya kasar nan, zaka samu sama da cibiyoyin kiwon lafiya 10,000, amma kalilan ne ke da kayan aiki, wasu ma ba a amfani da su."

Source: LEGIT.NG

TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

Related Posts

0 Response to "Da Dumi duminsa: Za a koma makarantun Islamiya a Kano"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?