--
Gwamnati za ta raba wa matasa rancen biliyan 75

Gwamnati za ta raba wa matasa rancen biliyan 75




Gwamnatin Tarayya ta fitar da Naira biliyan 75 don bai wa matasa bashin dogaro da kai.

Ministan Matasa da Wasannin, Sunday Dare ya bayyana haka a jawabin da ya yi wa ‘yan jarida a fadar shugaban kasa, ranar Laraba.

Dare ya ce, an kirkiri Bankin Matasa da zai taimaka wajen wayar da matasan Najeriya miliyan 68 masu shekara 18 zuwa 35 a kan harkar kasuwanci.

Ya kuma shawarci matasan da suke da tunanin wani kasuwanci da su tuntubi kananan bankuna da ke bayar da bashi guda 125 a fadin kasar nan don karbar jari ga wadanda suka cancanta.

Dare ya bayar da tabbacin cewa za a yi adalci ga matasan wajen gudanar da shirin da za a aiwatar ta fasahar intanet.

Ya ce kowa zai iya samu ba tare da bangarancin addini ko kabilanci ba.

SOURCE: https://aminiya.dailytrust.com.ng/

TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Gwamnati za ta raba wa matasa rancen biliyan 75"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?