--
Duba Yanda Sojoji suka kona makaranta da gidaje a jihar Taraba

Duba Yanda Sojoji suka kona makaranta da gidaje a jihar Taraba



An zargi sojojin Najeriya da kona gidajen mutane a garin Peva na karamar hukumar Takum a jihar Taraba.

Wasu mazauna garin sun shaidawa manema labarai na Punch cewa mutane na ta gudun tsira saboda wannan hari na bazata daga sojojin Najeriya.

Wani Mazaunin garin yace akwai wata makaranta me zaman kanta da wani mutum, Paul Gaza da sojojin suka lalata ta hanyar konawa da safiyar ranar, Asabar.

Sannan kuma sun kona gidajen wasu mutane. Shugaban kungiyar Kabikar Tiv reshen Takum, Peter Sule ya bayyana cewa sojojin sun taba yin irin wannan abu acan wani kauye

Yake idan masu laifi suke nema kamata yayi su kamasu amma su daina lalatawa mutane gine-ginen.  Da yake magana kan lamarin, kwamandan rundunar yankin, Janar Adeyemi Yekini ya bayyana cewa haka kawai sojoji ba zasu je su rika kona gidaje babu dalili ba.

Source: hutudole.com


TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Duba Yanda Sojoji suka kona makaranta da gidaje a jihar Taraba"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?