
Da duminsa: FG ta tsayar da ranar bude makarantun sakandire a cikin watan Agusta
Monday, 27 July 2020
Comment
Gwamnatin tarayya (FG) ta sanar da cewa za a bude makarantun sakandire a fadin kasa domin bawa daliban da ke shekarar karshe damar zana jarrabawar kammala karatun sakandire (WASSCE).
A cikin wata sanarwa da ma'aikatar ilimi ta fitar a yau, Litinin, ta bayyana cewa za a bude makarantun ne daga ranar Talata, 4 ga watan Agusta, 2020.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Ben Bem Goong, darektan yada labarai na ma'aikatar ilimi ta kasa.ATTENTION:— Federal Ministry of Education (@NigEducation) July 27, 2020
EXIT CLASSES TO REOPEN AUGUST 4TH, 2020
Secondary schools in the country are to reopen as from the 4th of August, 2020 for exit classes only. pic.twitter.com/2n9IctVA0O
A cewar sanarwar, an yanke shawarar bude makarantun ne bayan masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi sun shafe lokaci mai tsawo suna tattaunawa a ranar Litinin. Daliban da ke aji shidda; watau shekarar karshe, da takwarorinsu da ke aji uku ne kawai zasu koma makaranta, a cewar sanarwar.
SOURCE: LEGIT.NG
TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Da duminsa: FG ta tsayar da ranar bude makarantun sakandire a cikin watan Agusta"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?