
Da dumi duminsa: Daliban Najeriya ba za su rubuta WAEC ba a 2020 – FG
Wednesday, 8 July 2020
Comment
![]() |
MINISTAN ILIMI ADAMU ADAMU |
"Ina kira ga gwamnatocin jihohi da suka amince za su bude makarantu su sake shawara saboda halin da muke ciki na annobar COVID-19. Ina ganin akwai hatsari cikin yin hakan. Mu kare yaran mu," in ji shi.
Ya ce dukkan makarantun da ke karkashin gwamnatin tarayya za su cigaba da kasancewa a rufe har sai an tabbatar an ci galaba a kan cutar korona.
Ya ce ya gwammace daliban Najeriya su rasa shekarar karatu daya a maimakon jefa rayuwarsu cikin hatsari. Har wa yau, Ministan ya bayyana cewa za a yi wa dakunan kwanan daliban Kwallejin Fasaha ta Kaduna, Kadpoly, gyara. Ya ce wani mai saka hannun jari ne ya bayar da kudi N774,264,000 don yin gyaran. Ya tabbatar wa daliban kwallejin cewa gyaran ba zai saka ayi musu karin kudin dakunan kwanan ba.
SOURCE: LEGIT.NG
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Da dumi duminsa: Daliban Najeriya ba za su rubuta WAEC ba a 2020 – FG "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?