
An kori jami’in kwastan da ya ki karbar rashawar miliyan N180
Thursday, 23 July 2020
Comment
A sanarwar da kakakin hukumar DCP Joseph Attah ya fitar ta ce an dauki matakin a kan manyan hafsoshin ne bayan samun su da laifin sakaci da aiki a watan da ya gabata.
An tuhumi ACG Aminu Dahiru da hannu a badakalar fasakwaurin manyan motoci guda 295 makare da man fetur a watan Disamban 2019 a lokacin da yake aiki da Rundunar Kare kan Iyakokin kan Tudu na Kasa.
A watan Nuwamban shekarar 2019, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da Shugaban Hukumar Kwastam ta Najeriya, Hamid Ali suka karama Bashir Abubakar da lambar girmamawa bisa gaskiyarsa da kwazon aiki.
Bashir Abubakar ya kuma samu yabo daga hukumar a shekarar 2018 bayan da yaki karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka dubu 412 da wasu da suka shigo da miyagun kwayar Tramadol a lokacin da yake kula da rundunar a shiyar Apapa a Legas, lamarin da ya sa ya yi fice.
Kakakin hukumar ya kuma sanar tabbatar da nadin masu taimakawa shugaban rundunar guda biyar ta kuma yi wa manyan jami’anta 2,634 karin girma.
SOURCE: https://aminiya.dailytrust.com.ng/
TALLA: Sayi datar kowane network kamar: MTN, AIRTEL, GLO 9MOBILE mai inganci da rahusa latsa nan↓↓↓
Data Bundle Promo By BZ GLOBAL SERVICES
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
LATSANAN DOMIN SAMUN
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "An kori jami’in kwastan da ya ki karbar rashawar miliyan N180"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?