
Masu zanga-zanga sun lalata ofishin jakadancin Najeriya a Indonesia
Friday, 26 June 2020
Comment
Wasu daga cikinsu an hango suna lalata wata motar bas fara a harabar ginin ofishin jakadancin, yayin da wasu suka ragargaje kofofi da da tagogin ginin. Masu zanga-zangar sun kuma ciro tutar Najeriya da ke harabar ofishin jakadancin,
suna jan ta a kasa tare da yunkurin cinna mata wuta. Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, a cikin wasu sakonni har kashi biyu da ya wallafa a kan shafinsa na Twitter, ya yi Allah wadai da harin a ranar Alhamis, yana mai bayyana hakan a matsayin "abin kunya".
Wannan lamari ya sanya majalisar Wakilai ta ce dole ne Najeriya ta dauki mataki kan harin, domin irin wannan lamari ya fara wuce gona da iri. Da yake magana a ranar Talata, Femi Gbajabiamila, kakakin majalisar wakilan, ya ce nuna diflomasiya ta hanyar kawar da kai a kan lamarin ba zai magance matsalar ba. Kalli faifan bidiyon da jaridar The Cable ta wallafa a kan shafinta na Twitter:
— TheCable (@thecableng) June 25, 2020
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Masu zanga-zanga sun lalata ofishin jakadancin Najeriya a Indonesia "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?