
Kano:Ganduje ya bada umarnin yi wa masu mukami a gwamnatinsa gwajin miyagun kwayoyi
Friday, 26 June 2020
Comment
Garba ya ce za a fara gwajin dole daga cibiyar kula da magunguna. Gwamnatin Ganduje na kokarin gani ta yaki safara tare da ta'ammali da miyagun kwayoyi. Saboda haka ne ta kafa kwamitin yaki da hakan a jihar. "Gwamnan ya samar da shirye-shirye da za su tabbatar da an shawo kan matasalar amfani da miyagun kwayoyi.
Kamfanin Dillancin Labarai ya ruwaito cewa, majalisar dinkin duniya ta ware ranar 26 ga watan Yuni a matsayin ranar yaki da ta'ammali da miyagu kwayoyi da safararsu a fadin duniya. An ware ta ne don bayyana kokarinta wurin cimma manufar al'umma na yakar ta'ammali da miyagun kwayoyi. A wannan ranar ta shekarar nan, ana kokari wurin wayar da kai tare da ilmantar da jama'a don su gane matsalolin kwayoyi ga al'umma baki daya.
A wani labari na daban, rundunar 'yan sanda babban birnin tarayya da ke Abuja ta damke wasu mutum 24 da ake zargin su da laifukan da suka hada da amfani da sakon banki na bogi wurin biyan kayan da suka siya tare da biyan karuwan da suka yi lalata da su.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Kano:Ganduje ya bada umarnin yi wa masu mukami a gwamnatinsa gwajin miyagun kwayoyi "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?