
Ganduje ya kara rana guda a ranakun sassauta dokar kulle a jihar Kano
Sunday, 14 June 2020
Comment
ROHOTON:LEGIT.NG
Gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sanar da kara ranar Litinin a cikin jerin kwanakin da ake sassauta dokar kulle a jihar Kano.
Abba Anwar, babban sakataren yada labaran gwamna Ganduje, ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.
"Domin kara rage wahalhalun da jama'a ke fuskanta sakamakon bullar annobar korona, gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya amince da shigar da ranar Litinin a cikin jerin ranakun sassauta dokar kulle a fadin jihar Kano," a cewar anarwar.
A baya gwamnatin jihar Kano ta bawa jama'a damar fita tare da bude kasuwanni a ranakun Lahadi, Laraba da kuma Juma'a.
A cewar sabuwar sanarwar, "kara sassauta dokar kulle a ranar Litinin ya mayar da ranakun janye dokar kulle zuwa ranaku hudu a cikin sati.
"Daga yanzu jama'a zasu iya fita harkokinsu a ranar Litinin, kamar yadda suka saba a sauran kwanaki uku da suka saba, daga karfe 6:00 na safe zuwa karfe 6:00 na yamma.
"Ina kira ga jama'a da su cigaba da kiyaye dokokin kare yaduwar annobar korona.
"Jama'a zasu cigaba da saka takunkumin fuska, nesanta da junansu, amfani da sinadrin tsaftace hannu da yawan wanke hannu da sabulu," a cewar ganduje.
Kazalika, gwamna Ganduje ya ce ya zama wajibi kasuwanni da sauran wuraren taron jama'a su cigaba da daukan matakan kiyayewa domin ganin cewa an hana annobar korona samun sukunin yaduwa a tsakanin jama'ar jihar Kano.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Ganduje ya kara rana guda a ranakun sassauta dokar kulle a jihar Kano"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?