
Da dumi duminsa: Gwamnatin tarayya ta rage kudin aure a Najeriya
Tuesday, 30 June 2020
Comment
![]() |
ROHOTON PRESSLIVES: https://presslives.com/ |
Sabon kudin ya zo karkashin dokar aure ta CAP M6 LFN 2004, a cewar sanarwar da babban sakatare kuma mai rijistar aure a Najeriya, Georgina Ehuriah.
Wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ma’aikatar cikin gida ta Najeriya, Mohammed Manga, ta bayyana cewa hakan wani garambawul ne da gwamnati za tayi a fannin auren bayan samun shawarwari daga masu ruwa da tsaki a kwanan nan.
Lasisin yin aure a wuraren bauta an rage shi daga N30,000 na tsawon shekara biyu zuwa N6,000 a kowacce shekara.
Sabunta lasisin auren a wajen bauta, an amince a dinga biyan N5,000 a kowacce na tsawon shekara uku. Yayin da a da yake N30,000 kowacce shekara.
Hakanan an rage kudin daurin aure daga N21,000 zuwa N15,000, inda aka rage kudin lasisi na musamman daga N35,000 zuwa N25,000.
A kwanakin baya mun kawo muku rahoton fitacciyar jarumar fina-finan kudancin Najeriya na Nollywood, wacce ta bukaci a daina biyan kudin aure baki daya.
Toni Tones dai ta ce mata ba kadarori bane da za a ce duk lokacin da za ayi aure sai an biya musu sadaki ba. Ga dai cikakken labarin: Kamata yayi a haramta bayar da sadaki ga mata a lokacin aure – Toni Tones
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Da dumi duminsa: Gwamnatin tarayya ta rage kudin aure a Najeriya"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?