
Ma su gudu su gudu: Bidiyon yadda aka sha tsere bayan wani ya fadi a layin ATM
Monday, 4 May 2020
Comment
Rohoton: http://hausa.legit.ng
Jama'a sun ranta a na kare bayan wani mutum ya yanke jiki ya fadi yayin da ya ke amfani da na'urar ATM a wani banki a jihar Legas.
Gidan Talabijin na TVC ya rawaito cewa mutumin ya fadi, ya na numfashi sama - sama, a gaban na'urar ATM bayan layi ya zo kansa.
Jami'an tsaron bankin sun dauki mutumin zuwa cikin rumfa, kuma sun fuskanci akwai zazzabi mai zafi a jikinsa, lamarin da ya sa wasu kwastomomin bankin fecewa da gudu.
A yau, Litinin, ne umarnin shugaban kasa, Muhammadu Buhari, na sassauta kulle a jihohin Lagos, Abuja da Osun ya fara aiki.
Jama'a sun yi tururuwar fitowa bayan sun shafe kusan wata guda a cikin dokar hana zirga - zirga da walwala, wacce gwamnati ta saka domin dakile yaduwar annobar cutar covid-19.
Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 170 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar Litinin, 04 ga watan Mayu, 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 170 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
39-Lagos
29-Kano
24-Ogun
18-Bauchi
15-Kaduna
12-FCT
12-Sokoto
8-Katsina
7-Borno
3-Nasarawa
2-Adamawa
1-Oyo
NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Lahadi, 03 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 2558 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.
An sallami mutane 400 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 87.
Alkaluman NCDC na ranar Lahadi, 03 ga watan Afrilu, sun nuna cewa an samu raguwar mutanen da annobar ta harba idan aka kwatanta da alkaluman baya bayan nan da hukumar ta fitar.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
Jama'a sun ranta a na kare bayan wani mutum ya yanke jiki ya fadi yayin da ya ke amfani da na'urar ATM a wani banki a jihar Legas.
Gidan Talabijin na TVC ya rawaito cewa mutumin ya fadi, ya na numfashi sama - sama, a gaban na'urar ATM bayan layi ya zo kansa.
Jami'an tsaron bankin sun dauki mutumin zuwa cikin rumfa, kuma sun fuskanci akwai zazzabi mai zafi a jikinsa, lamarin da ya sa wasu kwastomomin bankin fecewa da gudu.
A yau, Litinin, ne umarnin shugaban kasa, Muhammadu Buhari, na sassauta kulle a jihohin Lagos, Abuja da Osun ya fara aiki.
Jama'a sun yi tururuwar fitowa bayan sun shafe kusan wata guda a cikin dokar hana zirga - zirga da walwala, wacce gwamnati ta saka domin dakile yaduwar annobar cutar covid-19.
At FCMB Onipanu in Lagos today, man started finding it difficult to breath and he collapsed while using ATM machine. When the the security men checked his temperature, it was alarming, bank customers took to their heels.#EaseOfLockdown pic.twitter.com/nt2DQJ82hF— TVC News (@tvcnewsng) May 4, 2020
Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 170 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar Litinin, 04 ga watan Mayu, 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 170 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
39-Lagos
29-Kano
24-Ogun
18-Bauchi
15-Kaduna
12-FCT
12-Sokoto
8-Katsina
7-Borno
3-Nasarawa
2-Adamawa
1-Oyo
NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:50 na daren ranar Lahadi, 03 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 2558 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a Najeriya.
An sallami mutane 400 bayan an tabbatar da samun saukinsu, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 87.
Alkaluman NCDC na ranar Lahadi, 03 ga watan Afrilu, sun nuna cewa an samu raguwar mutanen da annobar ta harba idan aka kwatanta da alkaluman baya bayan nan da hukumar ta fitar.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP
0 Response to "Ma su gudu su gudu: Bidiyon yadda aka sha tsere bayan wani ya fadi a layin ATM"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?