
Kowa da ranarsa: Tubabbun yan bindiga sun kwato mutane 12 daga hannun yan bindigan Zamfara
Thursday, 28 May 2020
Comment
ROHOTON: LEGIT.NG
Wasu ayarin tubabbun yan bindiga a jhar Zamfara sun ceto kimanin mutane 12 da wasu miyagun yan bindiga suka sace su, kuma tuni sun mika su hannun Yansanda. Punch ta ruwaito kakaakin rundunar Yansandan jahar, SP Muhammad Shehu ne ya bayyana haka, ina yace a ranar 27 ga watan Mayu ne tubabbun yan bindigan suka nuna bajinta.
“Kwamitin zaman lafiya na jahar Zamfara tare da hadin gwiwar tubabbun yan bindiga sun ceto mutane 12 daga hannun masu garkuwa da mutane. Kimanin makonni biyu da suka gabata aka yi garkuwa da mutane. “Amma Allah Ya kubutar da su ta hannun tubabbun yan bindiga da suka kai harin kwantan bauna kan miyagun yan bindigan da suka yi garkuwa da mutanen.” Inji shi.
A jawabinsa, kwamishinan Yansanda Usman Nagogo ya ce an samu nasarar ne sakamakon alkawarin da tubabbun yan bindigan suka dauka na taimaka wajen yakar abokansu. Don haka kwamsihinan ya jinjina ma kokarin tubabbun yan bindiga bisa amincewar da suka yi da tayin gwamnati da sauran hukumomin tsaro.
Daga karshe ya yi kira a gare su su cigaba da aikinsu yadda suka fara, sa’annan ya basu tabbacin hukumomin tsaro za su cigaba da aiki tare da su don tabbatar da zaman lafiya a jahar. A wani labari kuma, Jami’an hukumar DSS, ta sanar da kama mutumin da ya yi garkuwa da jikan fitaccen Malamin addinin Islama, Sheikh Dahiru Bauchi, mai shekaru 3 a duniya.
Punch ta ruwaito baya ga kama mutumin, jami’an na DSS sun kubutar da yaron cikin ruwan sanyi tare da kwato kudaden fansan da iyayensa suka biya don a sake shi. A ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu ne aka yi garkuwa da jikan a gidan Shehin dake jahar Kano. Shugaban hukumar DSS reshen jahar Kano, Muhammad Alhassan ya tabbatar da lamarin.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
Wasu ayarin tubabbun yan bindiga a jhar Zamfara sun ceto kimanin mutane 12 da wasu miyagun yan bindiga suka sace su, kuma tuni sun mika su hannun Yansanda. Punch ta ruwaito kakaakin rundunar Yansandan jahar, SP Muhammad Shehu ne ya bayyana haka, ina yace a ranar 27 ga watan Mayu ne tubabbun yan bindigan suka nuna bajinta.
“Kwamitin zaman lafiya na jahar Zamfara tare da hadin gwiwar tubabbun yan bindiga sun ceto mutane 12 daga hannun masu garkuwa da mutane. Kimanin makonni biyu da suka gabata aka yi garkuwa da mutane. “Amma Allah Ya kubutar da su ta hannun tubabbun yan bindiga da suka kai harin kwantan bauna kan miyagun yan bindigan da suka yi garkuwa da mutanen.” Inji shi.
A jawabinsa, kwamishinan Yansanda Usman Nagogo ya ce an samu nasarar ne sakamakon alkawarin da tubabbun yan bindigan suka dauka na taimaka wajen yakar abokansu. Don haka kwamsihinan ya jinjina ma kokarin tubabbun yan bindiga bisa amincewar da suka yi da tayin gwamnati da sauran hukumomin tsaro.
Daga karshe ya yi kira a gare su su cigaba da aikinsu yadda suka fara, sa’annan ya basu tabbacin hukumomin tsaro za su cigaba da aiki tare da su don tabbatar da zaman lafiya a jahar. A wani labari kuma, Jami’an hukumar DSS, ta sanar da kama mutumin da ya yi garkuwa da jikan fitaccen Malamin addinin Islama, Sheikh Dahiru Bauchi, mai shekaru 3 a duniya.
Punch ta ruwaito baya ga kama mutumin, jami’an na DSS sun kubutar da yaron cikin ruwan sanyi tare da kwato kudaden fansan da iyayensa suka biya don a sake shi. A ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu ne aka yi garkuwa da jikan a gidan Shehin dake jahar Kano. Shugaban hukumar DSS reshen jahar Kano, Muhammad Alhassan ya tabbatar da lamarin.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "Kowa da ranarsa: Tubabbun yan bindiga sun kwato mutane 12 daga hannun yan bindigan Zamfara "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?