
COVID-19: NCDC ta yi wa gwamnatin jihar Kogi martani
Friday, 29 May 2020
Comment
ROHOTON: LEGIT.NG
"Ba za mu amince da duk wani yunkurin tilasta mana bullar COVID-19 a jihar mu ba."
"A shirye muke mu kula da lafiyar mutanen jihar mu kuma ba mu da shawar yin siyasa da batun lafiyarsu," in ji shi. Gwamnatin ta Kogi ta ce mutane biyun da NCDC ta ce sun kamu da kwayar cutar ba yan jihar bane. Sai dai a yayin taron manema labarai na kwamitin yaki da COVID19 da ake gudanarwa kullum, Shugaban NCDC a Abuja ya yi watsi da ikirarin da gwamnatin Kogi ta yi. Ya ce babu wani kokwanto ko kuskure game da adireshin mutanen da aka yi wa gwaji daga jihar Kogi.
"Ba a samu wani matsala ba game da sakamakon mutum biyun da suka kamu. Sun bi kaidojin da aka shimfida. Cibiyar Lafiya ta Tarayya ce ta tura su Asibitin Kasa. Wannan shine tsarin da ake bi idan mutum ya kamu. "Likitocin da ke Asibitin Kasa sunyi zargin COVID19 ce bisa alamomin majinyatan. Sun aike da samfurin gwaji kuma an gwada sakamako ya nuna suna dauke da kwayar cutar. Mutanen biyu mazauna Kogi ne.
"Ana laakari da inda mutum ya ke zaune ne wurin bibiyar harkar lafiya irin wannan. An bi tsarin da ya dace. Bayan sakamakon sun fito an sanar da babban likita mai sanya ido kan cututtuka masu yaduwa. "Nauyi ya rataya a kan jihar ta gano wadanda suka yi cudanya da masu cutar. Muna fatar za su yi hakan," in ji shi.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
Twitter: https://twitter.com/bzglobalsevice
LATSANAN DOMIN SAMUN LABARI TA WHATSAPP: https://chat.whatsapp.com/KKAd5L0NolZ4F6yJqdblUO
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: https://www.appcreator24.com/app757657
0 Response to "COVID-19: NCDC ta yi wa gwamnatin jihar Kogi martani "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?