
Tagwayen Labarai: kyayatattun labarai guda biyar nayau karantasu
Friday, 24 April 2020
Comment
Mutum 684 ne suka rasa rayukansu sakamakon cutar korona a Birtaniya (Ingila, Scotland, Wales, Northern Ireland) cikin awa 24 da ta gabata, a cewar Sashen Lafiya.
Lissafin ya kama ne ya zuwa ranar Alhamis karfe 5:00 na yamma.
A gefe guda kuma, mutum 18,401 ne aka yi wa gwajin cutar kuma an gano 5,386 suna dauke da ita.
A hannu guda kuma kasar Saudiyya ta bayar da rahoton samun mutum 1,172 da suka harbu da cutar korona a cikin awa 24 da ta gabata, wanda ya kawo jumillar adadin zuwa 15,102.
Wasu 'yan biyu a Burtaniya sun mutu kwana uku a tsakani bayan gwaji ya nuna suna dauke da cutar korona, kamar yadda 'yar uwarsu ta bayyana.
Katy Davis mai shekara 37 ta mutu ranar Talata a babban asibitin birnin Southampton. Sai 'yar uwar tagwaitakarta Emma wadda tsohuwar ma'aikaciyar jinya ce, ta mutu da safiyar Juma'a, in ji 'yar uwarsu Zoe.
"Suna yawan cewa yadda suka zo duniya tare haka za su koma tare," In ji Zoe.
Musulmai da dama a fadin duniya sun sha ruwa a ranar farko ta azumin watan Ramadana.
Abin tambayar shi ne, yaya aka kai azumin - ganin yadda aka yi shi a cikin dokar zaman dabaro?
"Wannan azumin daban ne da ragowar (wadanda aka yi a baya), saboda haka dole ne a samu sauyin abubuwa" a cewar Dr Umar Bawa, malami a sashen koyar da addinin Musulunci a Jami'ar Bayero ta Kano.
Tauraruwar fina-finan Hausa na Kannywood, Rahama Sadau ta shawarci 'yan Najeriya da "mu tsare kanmu da kuma al'umma" baki daya daga cutar korona ta hanyar wanke hannu da sabulu na akalla dakika 20.
Sadau ta bayyana ne a wani bidiyo da hukumar NCDC ta shirya domin wayar da kan al'umma kan hadarin cutar da kuma yadda za su kare kansu.
Tauraruwar ta ce ta san jama'a sun tsorata da bullar cutar "saboda karancin bayani na yadda za mu killace kanmu," kodayake akwai hanyoyi da dama na kare kai daga cutar.
"Ku sani wanke hannu yana da matukar mahimmanci domin kuwa kashi 80% na yadda ake kamuwa da cutar (korona) daga musabaha ne," in ji Rahama.
"A wanke hannu da ruwa da sabulu akalla na dakika 20."
Taurarin fina-finai da na barkwanci da mawaka duk sun sha kiraye-kirayen wayar da kai a kasashen duniya game da cutar, wadda ta halaka sama da mutum dubu 290 a duniya kuma fiye da miliyan biyu da dubu 700 suka kamu.
Watch as actress @Rahma_sadau shares an important message on #COVID19 prevention in Hausa language— NCDC (@NCDCgov) April 24, 2020
She emphasises the importance of hand washing with soap under running water for 20 seconds to protect ourselves and our communities#TakeResponsibility pic.twitter.com/uWkrqtuB6z
An soke gasar kwallon kafa ta kasar Holland ba tare da fayyace kungiyar da ta lashe gasar ba.
Sannan kuma babu kungiyoyi da za su nitse kasa.
Matakin ya biyo bayan hukuncin gwamnati na haramta duk wani gagarumin buki saboda cutar Korona har sai zuwa 1 ga watan Satumba.
Hukumar da ke kula da gasar ta kasar Holland ta ce babu yadda za a yi a kammala gasa a kakar 2019 zuwa 2020.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP
0 Response to "Tagwayen Labarai: kyayatattun labarai guda biyar nayau karantasu "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?