
Sakon faifan bidiyon masu dauke da covid-19 ga sauran 'yan Najeriya
Wednesday, 1 April 2020
Comment
- Wasu daga cikin masu dauke da kwayar cutar covid-19 da aka killace a jihar Legas sun aiko muhimman sako a faifan bidiyo zuwa ga sauran 'yan Najeria
kuma aka killcesu a asibitin cututtuka masu yaduwa (IDH) da ke Yaba a jihar Legas, sun aiko sako a ciki faifan bidiyo domin fadakar wa tare da wayar da kan sauran 'yan Najeriya a kan kwayar cutar. Kazalika, masu dauke da kwayar cutar sun mika godiyarsu ga ma'aikatan lafiya, musamman likitoci da mataimakunsu, bisa dawainiyar da suke yi da su a yayin da suke a killace.
Bidiyon masu dauke da kwayar cutar, wanda gwamnan jihar Legas, Babjide Sanwo-Olu, ya fara wallafa wa a shafinsa na tuwita, ya cigaba da zagayawa a dandalin sada zumunta a ranar Laraba, 1 ga watan Afrilu, 2020.
Watching this #SomethingNewChallenge from the patients at one of our isolation centres made my day. They created the video to show that #COVID19 isnt a death sentence but must be taken seriously.— Babajide Sanwo-Olu (@jidesanwoolu) April 1, 2020
We thank our amazing health workers for their service. #StayHomeSaveLives pic.twitter.com/AiBA1GeJy8
A wani labarin da Legit.ng ta wallafa, wata karamar yarinya, mai shekaru 8 kacal a duniya, ta bayar da gudunmawar kudin domin a yaki cutar covid-19 a Najeriya. Karamar yarinyar, Vera Akpan, 'yar asalin jihar Delta, ta fasa bankinta na ajiyar kudi tare da rubuta wasika zuwa ga shugaban kasa,
Muhamnadu Buhari, domin tambayarsa a kan yadda za ta bayar da dukkan kudin ga gwamnatin tarayya. Ta bayyana cewa ta zabi bayar da kudin ne saboda bukatar kudade da gwamnati ke yi domin shawo kan annobar cutar COVID-19.
LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y
KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI
b
0 Response to "Sakon faifan bidiyon masu dauke da covid-19 ga sauran 'yan Najeriya"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?