--
Kaico! Jirgin yakin Najeriya ya yi ma kananan yara luguden wuta a jahar Borno

Kaico! Jirgin yakin Najeriya ya yi ma kananan yara luguden wuta a jahar Borno


Akalla mutane 17 ne suka mutu yayin da jirgin yakin Najeriya ya jefa bamabamai a kauyen Sakotoku dake karamar hukumar Dambo ta jahar Borno, bisa kuskure. Jaridar TheCable ta ruwaito wadanda suka mutu a wannan harin sune mata da kuma kananan yara, wanda suke wasa da zaman shan iska a karkashin wata bishiyar mangwaro.

Majiyoyi daga gidan Soja sun bayyana an jefa bamabaman ne bayan rundunar Sojan sama ta samu labarin taruwar yan Boko Haram a kauyen, don haka ta shirya musu luguden wuta. Inda ya kamata a kai harin shi ne wani yanki a Korongilum dake makwabtaka da Sakotoku da kimanin nisan kilomita 12, a nan ne mayakan Boko Haram din suka taru.

Kaico! Jirgin yakin Najeriya ya yi ma kananan yara luguden wuta a jahar Borno Source: Facebook 
“Bamu sani ba ko an samu gibi a musayar bayani ne tsakanin Sojojin sama da na kasa a lokacin da jiragen rundunar Sojin sama suka jefa bamabamai a kauyen ba, mutane 17 sun mutu, yawancinsu mata da kananan yara ne dake wasa a kasar bishiyar mangwaro. “Da dama kuma sun samu rauni, kuma an garzaya dasu zuwa asibitin runduna ta 25 dake Damboa, wadanda ke cikin mawuyacin hali kuma an mika su zuwa Maiduguri. Wadanda harin ya shafi gidajensu kuma sun zarce Damboa.” Inji majiyar.

A wani labari kuma, mutane 7 sun mutu a ranar 12 ga watan Afrilu yayin da yan ta’addan Boko Haram suka kai hari kwantan bauna a kan wasu motocin haya guda 2 a jahar Borno. Premium Times ta ruwaito Boko Haram ta tare motocin ne a wajen garin Auno, kimanin kilomita 20 daga garin Maiduguri, a kan babbar hanyar Maiduguri zuwa Damaturu. Wani matafiyi da ya yi ido hudu da gawarwakin ya bayyana cewa ya kirga gawarwaki guda 7 a wajen garin Auno, kuma an fada musu a daren jiya aka kai harin.KARANTA WASU LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/


LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP
https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y



KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI 






Domin Magana Damu Ko Bamu Shawara Ko Turo Mana Da Labari Ku Latsa Link Din Dake Qasa Domin Magana Damu Kaitsaye Ta whatsaapp👇👇👇
                            LATSA NAN COMIN MAGANA DAMU KAI TSAYE

KUSAUKE MANHAJAR LABARAI A WAYOYINKU NA ANDROID KYAUTA LATSA LINK DIN RUBUTUN DAKE QASA DOMIN YIN DOWNLOADING YANZU
https://www.appcreator24.com/app757657

Related Posts

0 Response to "Kaico! Jirgin yakin Najeriya ya yi ma kananan yara luguden wuta a jahar Borno "

Post a Comment

Tell us what you think about this article?