--
Dokar hana fita: An kama masu jana'izar karya a Kenya

Dokar hana fita: An kama masu jana'izar karya a Kenya




'Yan sanda a kasar Kenya da ke sa ido kan dokar hana fita sun kama wasu mutum hudu da suka yi badda-kama a matsayin masu jana'iza dauke da gawa a kan titin birnin Nairobi.

Sun bar babban birnin Nairobi kuma suka yi tafiyar kilomita 370 zuwa yamma da fankon akwatin gawa a motarsu kafin daga baya a kama su, a cewar ministan lafiya a ranar Asabar.

Kusan mako biyu kenan ba a shiga ba a fita a birnin Nairobi da kuma wasu yankuna uku da suka fi fama da cutar korona.

Rukunin masu sojan-gonar sun samu wuce wuraren ababen hawa da dama kafin wasu 'yan sandan gaza gani a Homa Bay County su bude akwatin gawar, in ji Ministan Lafiya Mutahi Kagwe.

Daga baya an gano direban motar yana dauke da cutar. Su ma sauran abokan tafiyar tasa an tsare su.

KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP

Related Posts

0 Response to "Dokar hana fita: An kama masu jana'izar karya a Kenya"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?