--
Covid-19: Za a killace dukkan 'yan majalisar dokokin Botswana

Covid-19: Za a killace dukkan 'yan majalisar dokokin Botswana



Za a killace dukkan 'yan majalisar dokokin Botswana 57 tsawon kwana 14 bayan wata nas da ke aiki a majalisar ta kamu da Covid-19.

Daraktan Lafiya na kasar Malaki Tshipayagae ya bayyana daukar wannan mataki, a cewa sakon Twtter da gwamnatin kasar ta wallafa.

Ranar Alhamis kasar ta sanar da karin mutum bakwai da suka kamu da coronavirus,cikinsu har da ma'aikaciyar lafiyar da ke aiki a majalisar dokokin.

Shi ma Shugaba Mokgweetsi Masisi ya halarci muhawarar da 'yan majalisar dokokin suka yi kan tsawaita dokar ta-baci zuwa wata shida.

Kwanan baya shugaban kasar ya kammala zaman killace kai da ya yi na kwana 14 bayan ya koma daga Namibia a watan Maris.

Botswana tana da mutum 13 da ke dauke da coronavirus.

KARANTA WASU LABARI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/

LATSA NAN๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡ DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP
https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y



KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI 






Domin Magana Damu Ko Bamu Shawara Ko Turo Mana Da Labari Ku Latsa Link Din Dake Qasa Domin Magana Damu Kaitsaye Ta whatsaapp๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡https://wa.me/2349066633320?text=Assalamu'alaikum%20Bz.%20Barka%20Da%20Aiki%F0%9F%A5%B0%F0%9F%A4%9D

KUSAUKE MANHAJAR LABARAI A WAYOYINKU NA ANDROID KYAUTA LATSA LINK DIN RUBUTUN DAKE QASA DOMIN YIN DOWNLOADING YANZU
https://www.appcreator24.com/app757657

0 Response to "Covid-19: Za a killace dukkan 'yan majalisar dokokin Botswana"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?