
An samar da wurin gwajin cutar korona a Sokoto da Zaria
Saturday, 25 April 2020
Comment
Hukumar da ke yaki da cututtuka masu yaduwa a Najeriya NCDC ta sanar da karin wuraren gwajin cutar korona guda biyu a Najeriya.
A sanarwar da ta wallafa a Twitter, hukumar ta ce za a iya gwajin cutar a asibitin koyarwa na Jami'ar Usman Danfodio a Sokoto da kuma asibitin koyarwa na Jami'r ahmadu Bello da ke Zaria.
Hukumar ta ce yanzu tana da cibiyoyin gwajin cutar korona 15.
We’re proud to announce the inclusion of 2 new labs to the molecular laboratory network for #COVID19 at— NCDC (@NCDCgov) April 25, 2020
🧪Usman Danfodio University Teaching Hospital, Sokoto
🧪Ahmadu Bello University, Zaria, Kaduna
This brings the number of labs with capacity to test for #COVID19 to 15 pic.twitter.com/HEzLh7U739
Awani Labarin Kuma: Adadin wadanda suka mutu a Birtaniya ya wuce 20,000
Sashen kula da jama'a na Birtaniya ya ce wasu mutum 813 sun mutu a asibitocin kasar sakamakon cutar korona.
Yanzu jumillar adadin ya zama 20,319 - wannan ya sa Birtaniya ta zama kasa ta biyar da take da fiye da mutum 20,000 da suka rasa rayukansu, tare da Italiya da Spaniya da Faransa da Amurka.
KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com
KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/
KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/
KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP
0 Response to "An samar da wurin gwajin cutar korona a Sokoto da Zaria"
Post a Comment
Tell us what you think about this article?