--
An nada Buhari jagoran yaki da cutar korona

An nada Buhari jagoran yaki da cutar korona

Shugabannin kasashe mambobin kungiyar Habaka Tattalin Arzikin Afirka ta Yamma, ECOWAS sun nada Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya a matsayin jagoran yaki da cutar korona a yankin.

An zabe shi ne a ranar Alhamis a wani taro da suka gudanar ta bidiyo karkashin jagorancin Shugaban Nijar kuma shugaban kungiyar Mahamadou Issoufou, kamar yadda fadar shugaban ta bayyana a shafinta na Twitter.

Buhari zai jagoranci bullowa tare da aiwatar da dukkanin matakan da za a dauka kan yaki da cutar a yankin da ya kunshi kasashe 15, ciki har da Najeriya da Nijar da Ghana da Gambia da Mali da Senegal da Saliyo.

Sauran sun hada da Benin da Ivory Coast da Liberia da Cape Verde da Togo da Burkina Faso da Guinea da Guinea Bissau.

"A cikin kowanne irin yanayi kamar wannan, akwai damarmaki," in ji Shugaba Buhari.

"Saboda haka wajibi ne mu nemo wadannan damarmaki da wannan yanayin maras dadi zai ba mu ta hanyar aiwatar da matakai, wadanda kafin yanzu, zai yi wuya mu iya daukarsu."


KU AIKO MANA DA LABARI KO SHAWARWARI KO MAGANA DAMU KAITSAYE TA ADRESHIN EMAIL: bzglobalservicelabari@gmail.com

KARANTA WASU SABBIN LABARAI ANAN: https://www.bzglobalservice.com.ng/

KU BIYOMU A: https://web.facebook.com/Bzglobalservice.com.ng/

KU SAUKE MANHAJARMU TA ANDROID APPLICATION AWAYOYINKU NA HANNU KYAUTA DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI: BZGLOBALSERVICE.COM.NG APP

0 Response to "An nada Buhari jagoran yaki da cutar korona"

Post a Comment

Tell us what you think about this article?