
Tube rawanin Sanusi: Dattjan Kano sun yi wa Ganduje zazzafan martani
Monday, 9 March 2020
Comment
Kungiyar dattijan jihar Kano ta kalubalanci sauke Sanusi Lamido a matsayin sarkin Kano da Gwamnan Abdullahi Ganduje yayi. Sun kuma yi alkawarin daukar mataki a kan abinda gwamnatin jihar tayi. Idan zamu tuna, gwamnan ya fitar da takarda a ranar Litinin ta hannun sakataren gwamnatinsa,
Tube rawanin Sanusi: Dattjan Kano sun yi wa Ganduje zazzafan martani Source: Twitter
“Mu dattijan Kano mun fada tsananin damuwa da fargabar takardar da sakataren gwamnatin jihar kano ya karanta mai bayyana tube rawanin Mai martaba, Muhammadu Sanusi II a matsayin gwamnan jjihar Kano. “A sakamakon wannan abun alhinin da Gwamnan Ganduje yayi, muna kira ga Kanaawa da su kwantar da hankulansu don hargitsi ba zai samar da mafita ba.
“Mun yarda da ikon Allah kuma zamu ci gaba da amincewa da duk abinda ya kaddara. Shi ke da mulki,” takardar ta ce. “Duk da haka, za mu kalubalanci wannan lamarin ta halastacciyar hanya. A takaice dai zamu bibiyi shari’armu da ke kalubalantar majalisar jihar Kano din karkashin Gwamnan wacce ta tumbuke sarkin,” cewar takardar.
LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y
KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI
0 Response to "Tube rawanin Sanusi: Dattjan Kano sun yi wa Ganduje zazzafan martani "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?