
COVID-19: abinda Dangote ya fada bayan sakamakon gwajinsa ya fito
Sunday, 29 March 2020
Comment
Attajirin dan kasuwa, Aliko Dangote, ya sanar da cewa sakamakon gwajin da aka yi masa ya nuna cewa ba ya dauke da kwayar cutar COVID-19. An ji tsoton cewa Dangote zai iya kamuwa da kwayar cutar coronavirus bayan ya yi mu'amala da Abba Kyari,
shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa da aka tabbatar da cewa yana dauke da kwayar cutar. A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na tuwita, Dangote ya bayyana cewa ya yi gwajin ne a matsayinsa na dan kasashe da dama sannan shugaba a kasuwanci. Ya ce yana jagorantar shugabannin a bangaren kasuwanci domin taimakon gwamnati a kokarinta na dakile yaduwar cutar. Dangote ya bayyana cewar annobar cutar coronavirus ta taba lafiyar jama'a da sauran harkokinsu.
The COVID-19 pandemic has significantly disrupted modern society, affecting our collective health and well-being. As a global citizen and business leader, I took the COVID-19 test and the result came back NEGATIVE. (1/2)— Aliko Dangote (@AlikoDangote) March 29, 2020
A ranar Lahadi ne kasar Andolus (Spain) ta sanar da mutuwar mutane 838 sakamakon kamuwa da kwayar cutar coronavirus.CACOVID(Coalition Against COVID-19) is an initiative that I am leading with other private sector leaders&our common goal is to support ongoing Government initiatives with our resources in the fight against Covid-19. We are in this together & I am optimistic we will overcome.(2/2)— Aliko Dangote (@AlikoDangote) March 29, 2020
Ya zuwa yanzu, kwayar cutar coronavirus ta kashe mutane fiye da 30,000 a fadin duniya a karshen makon nan. Kwayar cutar ta fi gigita kasar Amurka da yankin nahiyar turai a 'yan kwanakin baya bayan nan.
A wata kididdiga da jami'ar 'Johns Hopkins' ta gudanar, ta bayyana cewa mutane 30,800 ne kwayar cutar COVID-19 ta halllaka a fadin duniya, yayin da take cigaba da mamaya da karya tattalin arzikin mutane da na kasashe. Mutane fiye da 20,000 ne kwayar cutar ta hallaka a iya yankin nahiyar turai. Kwayar cutar ta kashe mutane fiye da 1400 a rana daya a kasar Spain da Italy.
LATSA NAN👇👇👇 DOMIN SAMUN LABARAI DA DUMI DUMI TA WHATSAPP https://chat.whatsapp.com/BztTOlXx6c183yYthtZq1Y
KU BIYOMU TA FACEBOOK FAGE DINMU KUYI LIKE DOMIN SAMUN LABARI
b
0 Response to "COVID-19: abinda Dangote ya fada bayan sakamakon gwajinsa ya fito "
Post a Comment
Tell us what you think about this article?